2019-07-30 09:32:43 cri |
Sanarwar da kakakin rundunar kawancen Col. Timothy Antigha ya fitar, ta ce soja guda ya rasa ransa yayin musayar wuta da suka yi da mayakan. Kana wasu sojojin 5 sun ji rauni.
Dakarun kawancen sun hada da na kasashen Nijeriya da Chadi da Kamaru da kuma Benin.
A cewar Kakakin, rundunar za ta ci gaba da hada gwiwa da jami'an tsaron kasar wajen ci gaba da daukar matakan da suka wajaba na tabbatar da cimma burinta a yankin tafkin Chadi.
Ya ce za su kara matsa kaimi ta yadda ayyukansu zai hada da kai samame, da kwanton bauna da sintiri domin fatattakar 'yan ta'adda daga tungarsu a yankin tafkin Chadi. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China