Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Wang Qishan ya halarci bikin bude taron dandalin tattaunawa kan kiyaye zaman lafiya na duniya karo na 8
2019-07-08 14:15:13        cri
An gudanar da taron dandalin tattaunawa kan kiyaye zaman lafiya na duniya karo na 8 mai taken "yin kokari da hadin gwiwa da more fasahohi wajen tabbatar da dokokin kasa da kasa", inda mataimakin shugaban kasar Sin Wang Qishan ya halarci bikin tare da gabatar da jawabi.

A cikin jawabinsa, Wang Qishan ya bayyana cewa, Sin ta sa kaimi ga kafa sabuwar dangantakar dake tsakanin kasa da kasa da raya al'umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil'adama, da tabbatar da ra'ayin bangarori daban daban, da fadada hanyoyin samun bunkasuwa tare, da yin mu'amalar al'adu da juna, don tinkarar sabon kalubale dake gaban dan Adam tare. Kana Sin ta yi kira ga kasa da kasa su kiyaye tunanin samun bunkasuwa cikin lumana, da sa kaimi ga raya tattalin arzikin duniya bisa tsarin bai daya, da kuma kafa dokokin kasa da kasa mai adalci da dacewa tare. (Zainab)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China