Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Wang Yi ya gana da wasu jami'an kasashen Afirka
2019-06-26 11:17:49        cri
Memba a majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi ya gana da wasu manyan jami'an kasashen Afirka wadanda suka zo birnin Beijing don halartar taron tabbatar da sakamakon da aka cimma a taron kolin FOCAC, ciki har da ministocin harkokin wajen kasashen Zimbabwe da Lesotho da Kwadibwa da Equatorial Guinea da Ghana da Uganda da Libya gami da ministan kula da tattalin arziki na jam'iyyar PFDJ ta kasar Eritrea.

A yayin ganawar, Wang Yi ya bayyana cewa, yayin da kasar Sin ke mu'amala da kasashen Afirka, tana mara musu baya wajen kare ikon mallakar kasa da tabbatar da zaman lafiya gami da neman ci gaba. Haka kuma Sin na nuna goyon-baya ga kasashen Afirka wajen kara taka muhimmiyar rawa a harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya, tare kuma da kare hakkokin kasashen Sin da Afirka da na sauran wasu kasashen dake tasowa.

Wang ya ce, makasudin shirya taron tabbatar da sakamakon da aka cimma a taron kolin FOCAC, wato dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar Sin da Afirka shi ne, kara tuntubar juna tsakanin Sin da Afirka da cimma daidaito da kara dankon zumunci tsakaninsu.

A ranar kuma, memba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin Yang Jiechi ya gana da wasu ministocin harkokin waje na kasashen Afirka, ciki har da na Saliyo da Equatorial Guinea da Afirka ta Kudu da Senegal.(Murtala Zhang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China