Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
An rufe taron ministocin kudi da shugabannin bankunan tsakiya na kasashen G20 a kasar Japan
2019-06-10 12:53:05        cri
An rufe taron ministocin kudi da shugabannin bankunan tsakiya na kasashen G20 na kwanaki 2 a birnin Fukuoka dake kasar Japan a jiya Lahadi, inda aka tattauna batutuwa game da yanayin tattalin arzikin duniya, da samar da kudi don raya ci gaba, da harajin kasa da kasa, da rashin daidaito a duniya, da karin yawan tsofaffi, da zuba jari ga ayyukan more rayuwa, da yin kwaskwarima kan hukumomin hada-hadar kudi da sauransu.

Ministan kudi na kasar Sin Liu Kun ya halarci taron tare da yin jawabi, inda ya yi nuni da cewa, an kara samun rashin tabbaci a fannin raya tattalin arzikin duniya a halin yanzu, ana fuskantar ra'ayin bada kariya ga cinikayya a duniya. Ya kamata bangarori daban daban su sa lura kan hadarin koma bayan tattalin arziki, da tabbatar da tsarin bangarori daban daban bisa ka'idoji, da warware matsaloli cikin adalci yadda ya kamata. A halin yanzu, an samu rashin daidaito a kasashe da suka ci gaba, ya kamata wadannan kasashe su kara taka muhimmiyar rawa a wannan fanni. Daukar matakan bada kariya ga cinikayya a tsakanin bangarori biyu ba su taimakawa daidaita matsalar rashin daidaito kan tsarin bangarori daban daban ba, kana za su kawo illa ga samun bunkasuwar tattalin arzikin duniya. Sin ta kiyaye samun bunkasuwar tattalin arziki a bana. Gwamnatin kasar Sin za ta dauki wasu matakan yin kwaskwarima da bude kofa ga kasashen waje don sa kaimi ga bude kofa da samun bunkasuwar tattalin arziki mai inganci, da kuma samun wadata a duniya baki daya. (Zainab)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China