2019-06-06 20:49:50 cri |
Yau Alhamis 6 ga wata, jami'in ofishin hukumar kula da aikin tsara harajin kwastam ta majalisar gudanarwar kasar Sin ya ce, "Mun lura cewa, ofishin wakilin tattauna cinikayya na Amurka ya sanar da cewa, zai ci gaba da kara buga harajin kwastam ga kayayyakin da suka bar kasar Sin kafin ranar 10 ga watan Mayun bana, kuma za su shiga kasar Amurka kafin ranar 15 ga watan Yunin shekarar nan, da kaso 10 bisa dari", game da hakan, jami'in ya bayyana cewa, matakin da Amurka ta dauka ba zai canja yunkurinta, na kara harajin tun daga ranar 10 ga watan Mayun bana ba.(Jamila)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China