Hukumomin a kasar Sri Lanka, sun ce hare-haren da aka kai kasar yau Lahadi, sun yi sanadin mutuwar mutane 192 tare da jikkata wasu sama da 470, inda kuma aka sanya dokar takaita zirga-zirga a fadin kasar.
Jimilar hare-hare 8 aka kai kasar kawo yanzu, inda aka kai 6 da safe, wasu 2 kuma da rana. An ayyana dokar takaita zirga zirgar ne daga karfe 6 na yammacin yau, zuwa karfe 6 na safiyar gobe Litinin. (Fa'iza Msutapha)