in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar harkokin wajen Sin: Kafa ma'aunin tsaron Intanet ba tare da rufa-rufa ba shawara ce mai ma'ana
2019-03-06 21:00:41 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yau cewa, kafa ma'aunin tsaro na kafar Intanet ta hanyar da ta dace kuma ba tare da rufa-rufa ba, wata kyakkyawar shawara ce mai ma'ana.

Rahotanni na cewa, a kwanakin baya ne, firaministan kasar Portugal Antonio Costa ya zanta da jaridar Financial Times ta kasar Ingila, inda ya jaddada cewa, bai kamata ba kasashen kungiyar tarayyar Turai su wuce gona da iri a fannin binciken tsaro don nuna bambancin ra'ayi ga jarin da kasashen da ba na EU ba suka zuba. Kasar Portugal ta fahimci damuwar da wasu kasashe suka nuna game da hadarin dake tattare da yin hadin-gwiwa da kamfanin Huawei wajen amfani da fasahar sadarwar 5G, amma a ganinta, bai kamata a dakatar da ayyukan zamanintar da harkokin sadarwa a kasashen Turai ba.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ga wasu
v Sin ta yi Allah wadai da harin Afghanistan 2016-07-25 11:26:32
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China