in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan Zimbabwe: CIIE ya shaida wa duniya manufar bude kofa ta Sin
2018-11-13 13:38:19 cri
Ministan masana'antu da cinikayya na kasar Zimbabwe Mangaliso Ndlovu ya bayyana wa 'yan jarida jiya a birnin Harare cewa, bikin baje kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin wato CIIE, ya shaida wa duniya manufar bude kofa ga kasashen waje da kasar Sin take bi, wanda zai sa kaimi ga kamfanonin Zimbabwe su kara fadada kasuwarsu a kasar Sin.

Ndlovu ya bayyana cewa, an yi maraba sosai ga tawagar kasar Zimbabwe da ta halarci bikin CIIE na Shanghai, yana mai godiyawa mashirya bikin. A ganinsa, bikin CIIE ya shaida imanin Sin na bude kofa ga kasashen waje, yana mai cewa, a karkashin yanayin tsananta rikicin ciniki na duniya da ra'ayin ba da kariya ga cinikayya, bikin CIIE ya shaida wa duniya manufar Sin ta bude kofa ga kasashen waje, don haka bikin CIIE muhimmin biki ne.

Game da yanayin fitar da kayayyaki daga kasar Zimbabwe zuwa kasar Sin kuwa, Ndlovu ya bayyana cewa, ko da an gudanar da tattaunawa yayin bikin CIIE, ana bukatar kamfanonin kasar Zimbabwe su kara yin kokarin fadada kasuwarsu a kasar Sin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China