in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ganawar shugaba Xi da Trump yayin taron G20 za ta yi matukar alfanu inji Yang Jiechi
2018-11-10 15:42:26 cri
Mamba a ofishin hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS Yang Jiechi, ya ce ko shakka ba bu ganawar da aka tsara yi yayin taron kungiyar G20 a kasar Argentina, tsakanin shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Donald Trump, za ta haifar da matukar fa'ida ga kasashen.

Mr. Yang Jiechi, ya bayyana hakan ne a jiya Juma'a, yayin taron manema labarai da ya gudana, bayan kammala taro na biyu, na wakilan Sin da Amurka game da harkokin diflomasiyya da tsaron kasashen.

Ya ce ya dace Sin da Amurka su fadada tattaunawa, tare da ci gaba da cudanya, da wanzar da shirye shirye, na tabbatar da nasarar ganawar shugabannin.

Mr. Yang, da sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo, da sakataren tsaron Amurka James Mattis ne suka jagoranci taron. Kaza lika taron ya samu halartar dan majalissar zartaswar Sin, kuma ministan tsaron kasar Wei Fenghe. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China