in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci Amurka da ta daina keta ikon mulkin ta
2018-10-16 19:11:30 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya furta a yau Talata cewa, kasar Sin tana da cikakken ikon mallakar wasu tsibirai dake tekun kudancin ta, da kuma yankunan teku dake kewayen tsibiran. Don haka kasar ta bukaci Amurka da ta daina daukar matakai, na keta ikon mulkin ta, da lalata moriyarta a fannin tsaro.

Kafin haka, wani babban jami'in kasar Amurka ya ce, kasar Sin na yunkurin jibge karin sojoji a yankin tekun kudancin kasar, gami da haifar da matsala ga wani jirgin ruwan sojan kasar Amurka, dake aiwatar da 'yancinsa na zirga-zirga a yankin tekun.

Game da hakan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lu Kang, ya ce, wannan batu karya ce zalla, kuma yunkuri ne na shafa wa kasar Sin kashin kaza. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China