in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ambaliyar ruwa ta kashe mutane 10, ta raba daruruwa da gidajensu a Najeriya
2018-09-14 10:41:05 cri
Akalla mutane 10 ne aka tabbatar da mutuwarsu kana wasu daruruwa suka rasa muhallansu a sanadiyyar ambaliyar ruwa a jihar Adamawa dake shiyyar arewa maso gabashin Najeriya, in ji wani jami'in yankin.

Jami'in hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Muhammed Suleiman, ya shedawa 'yan jaridu cewa, gonaki masu yawa ne ambaliyar ruwan ta lalata a jihar wanda ruwan sama da aka sheka kamar da bakin kwarya ne ya haddasa ambaliyar.

A cewar Suleiman, al'ummomi masu yawa daga kananan hukumomi 9 ne ke zaune a kusa da gabar kogin Benue, wanda shi ne kogi na biyu mafi girma a Najeriya, inda kuma a can ne ambaliyar ruwan ta shafa.

A halin yanzu fiye da rabin jama'ar jihar na fuskantar barazanar yiwuwar ambaliyar ruwa.

Mazauna yankin sun tafka hasarar daruruwan dabbobinsu kamar shanu, a sanadiyyar ibtila'in.

Jami'in ya ce, hasarar da ake samu tana kara kamari, kuma ambaliyar ruwan ta zama wani babban kalubale wanda ke yin barazana ga harkokin noma a jihar dake shiyyar arewa maso gabashin Najeriya. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China