in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan wajen Sin ya aike da sakon ta'aziyyar rasuwar Kofi Annan
2018-08-21 20:07:18 cri

Dan majalissar zartaswar kasar Sin, kuma ministan wajen kasar Wang Yi, ya aike da sakon ta'aziyya game da rasuwar tsohon babban magatakardar MDD Kofi Annan.

Cikin sakon nasa da ya aike a ranar 19 ga watan Agustar nan, ga babban magatakardar MDD Antonio Guterres, da kuma ministan harkokin wajen Ghana Shirley Ayorkor Botchwey, Mr. Wang ya bayyana matukar alhinin rasuwar Mr. Annan, yana mai gabatar da ta'aziyya ga iyalan sa.

Tsohon magatakardar MDDr, wanda kuma ya taba samun lambar yabo ta Nobel game da zaman lafiya, ya rasu ne a ranar Asabar yana da shekaru 80.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China