in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi ya aikewa takwaransa na Pakistan sakon ta'aziya dangane da harin ta'addancin da aka kai kasar
2018-07-15 20:18:18 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya aikewa takwaransa na Pakistan Mamnoon Hussain sakon ta'aziya dangane da mummunan harin ta'addacin da aka kai a kasar.

A cikin sakon, shugaba Xi ya kuma mika ta'aziya ga iyalan wadanda harin ya rutsa tare da jajantawa iyalan wadanda suka jikkata. Xi ya ce ta'addanci babban makiyin bil-adam ne, kuma kasar Sin ba ta goyon bayan duk wani nau'i na ta'addanci, kana ta yi Allah wadai da harin ta'addancin da aka kai a kasar Pakistan.

Shugaba Xi ya ce, har kullum Sinawa na tare da al'ummar Pakistan, suna kuma goyon bayan matakan da kasar ke dauka na yaki da ayyukan ta'addanci, da tabbatar da zaman lafiya da kare rayukan al'umma. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China