in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya yabawa matakin cimma zaman lafiya tsakanin Eritrea da Ethiopia
2018-06-22 12:19:03 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya ce a shirye yake, ya taimakawa Eritrea da Ethiopia, biyo bayan bullowar batun neman sulhu tsakanin makwabtan kasashen dake kahon Afrika.

Wata sanarwa da kakakinsa ya fitar jiya, ta ruwaito Sakatare Janar din na maraba da matakan da aka dauka na warware sabanin dake tsakanin kasashen biyu.

A wannan watan ne, Ethiopia ta sanar da shirinta na amincewa da kuma aiwatar da yarjejeniyar kan iyaka ta 2002, da ta kawo karshen rikicin da aka shafe shekaru 2 ana yi tsakanin kasashen, wanda ya yi sanadin mutuwar dubban mutane. Idan babu yarjejeniyar, za a ci gaba da gwabza fada, inda ake zargin Eritrea da kasancewa cikin shirin yaki.

A wani jawabi da ya yi a wannan makon, Shugaban Eritrea Isaias Afwerki, ya sanar da shirinsa na tura wakilai zuwa Addis Ababa, domin nazarin halin da ake ciki da kuma tattaunawa kai tsaye tare da tsara matakan da za a dauka a nan gaba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China