in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi tur da harin yan bindigar Sudan ta kudu dake yankin Gambela na kasar Habasha
2016-04-19 13:46:14 cri
Shugabar kuniyar tarayyar Afrika AU Nkosazana Dlamini-Zuma, ta yi Allah wadai game da kaddamar da harin da yan tawayen Sudan ta kudu suka yi a yankin Gambella dake kasar Habasha.

Dlamini, ta bayyanar harin da cewar mummunan laifi ne da 'yan tawayen na Sudan ta kudu suka kaddamar a Jakawa dake yankin Gambella na kasar Habasha a ranar 15 ga watan Aprilun 2016, wanda yayi sanadiyyar hallaka mutane 208 da kuma yin garkuwa da wasu 102 wadanda mata ne da kananan yara.

AU ta aike da sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda harin ya rutsa dasu, da fatan samun sauki ga wadan suka jikkata.

Sannan ta bada tabbacin goyon bayan AU ga gwamnatin Habasha da alummar kasar.

Dlamini-Zuma ta bukaci da'a gaggauta sako mata da kananan yaran da aka yi garkuwa dasu ba tare da gindaya wasu sharruda ba.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China