in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya aike da sakon taya murna ga taron shugabannin kotunan kolin kasashen dake amfani da harshen Portugal
2018-03-26 13:47:18 cri
An bude taron shugabannin kotunan koli na kasashen dake amfani da harshen Portugal a yau Litinin a birnin Guangzhou na kasar Sin, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da wasikar taya murna.

A cikin wasikar, Xi ya nuna cewa, taron na da ma'ana kwarai wajen inganta cudanya da hadin kai tsakanin kasar Sin da kasashen dake amfani da harshen Portugal a fannin dokokin shari'a, wanda zai samar da muhalli mai kyau ga bangarorin biyu wajen samun ci gaba tare.

Baya ga haka, Xi ya bayyana fatan wakilai mahalartan taron za su yi cudanya tare da tattaunawa sosai, don inganta gudanar da harkokin kasa da kasa da martaba da doka da oda ta hanyar yanar gizo. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China