in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi: bude kofar kasar Sin ga kasashen waje moriya ce ga dukkan sassa
2017-10-31 10:07:22 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ce manufar kasar Sin ta bude kofa ga kasashen waje, lamari ne da zai ci gaba da haifar da alfanu ga daukacin sassan duniya.

Shugaban wanda ya yi wannan tsokaci, yayin ganawar sa da mambobin hukumar bada shawarwari na jami'ar Tsinghua a babban dakin taruwar jama'a dake nan birnin Beijing a jiya Litinin, ya ce Sin na tallafawa ci gaban tattalin arzikin duniya, wanda hakan ya zamo hanyar cimma moriya gare ta, da ma sauran kasashen duniya.

Da ya tabo batu game da taron wakilan JKS na 19 da ya kammala 'yan kwanakin baya, shugaban na Sin ya ce taron ya yi matukar armashi, ya kuma dada haskaka kwarin gwiwar da Sin ke da shi, game da aiwatar da manufofin gurguzu mai halayyar musamman ta kasar Sin.

Shugaba Xi ya kara da cewa, kasar sa za ta ci gaba da gudanar da sauye sauye a dukkanin fannoni, tare da tabbatar da tsaron kasa, da 'yancin mulkin kai, da ci gaba mai dorewa.

Ya ce basira jigo ce ta kirkire kirkire, kuma za a iya gina ta ne kadai, idan aka ilmantar da al'umma yadda ya kamata.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China