in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude wani muhimmin taron tuntuba game da batutuwan da suka shafi kahon Afrika a Khartoum
2017-10-09 09:32:58 cri
An bude wani muhimmin taron tuntuba kan batutuwan da suka shafi yankin kahon Afrika jiya Lahadi a birnin Khartoum, wanda Tarayya Afrika da hadin gwiwar kungiyar raya kasashen yankin gabashin Afrika da gwamnatin Sudan suka shirya.

Da yake jawabi ga taron, ministan harkokin wajen Sudan Ibrahim Ghandour, ya ce manufar taron ita ce, tattaunawa da amincewa da ingantattun hanyoyi da dabarun da za su samar da tsaro da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaba ga al'ummomi da kasashen dake yankin kahon Afrika.

Ya ba da misali da kalubalen da yankin ke fuskanta da suka hada da yakin basasa da rikice-rikicen siyasa da barkewar annobar cututtuka da rashin kyakkyawan tsarin kasa da bullowar kungiyoyin masu kaifin ra'ayin addini da kuma gasar kasa da kasa kan albarkatu.

A nasa bangaren, shugaban kwamitin aiwatar da manufofi na Tarayya Afrika Thabo Mbeki, ya jadadda muhimmancin warware batutuwan dake ci wa yankin kahon Afrika tuwo a kwarya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China