in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana fatan kasashen dake yankin kahon Afirka za su inganta hadin gwiwa tsakaninsu
2016-11-11 11:00:52 cri
Jiya Alhamis mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Wu Haitao ya bayyana cewa, yankin kahon Afirka wanda ya kunshi kasashen yankin arewa maso gabashin nahiyar, yanki mai muhimmanci a nahiyar Afirka. A saboda haka, samar da zaman lafiya a wannan yanki yana da matukar muhimmanci ga tabbatar da moriyar kasashen dake wannan yanki. Wannan ya sa, kasar Sin take fatan kasashen za su ciyar da hadin gwiwar dake tsakninsu gaba, a kokarin da ake yi na warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari yadda ya kamata.

A jiya ne, aka kada kuri'u kan ko za a tsawaita takunkumin da aka kakabawa kasashen Somaliya da Eritrea, inda aka zartas da kudurin tare da samun kuri'un amincewa guda 10, yayin da mambobi guda biyar ba su jefa kuri'un ba, ciki har da kasar Sin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China