in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya ta kaddamar da shirin yaki da haramtattun kwayoyi
2017-06-29 09:25:05 cri

Ma'aikatar lafiya ta kasar Kenya ta kaddamar da wasu ka'idoji domin tantance sinadaren da ake amfani da su domin dakile karuwar ta'ammali da haramtattun kwayoyi dake ci gaba da yin kamari a kasar

Daraktan sashen kula da magunguna na kasar Jackson Kioko, ya fada cewa, yawan amfani da haramtattun kwayoyi a kasar yana ci gaba da ta'azzara musamman a tsakanin matasan kasar.

Ya yi gargadin cewar, yawaitar ta'ammali da haramtattun kwayoyin babbar barazana ce da ka iya yin nakasu wajen samun nasarar shirin nan na muradin ci gaban kasar nan da shekara ta 2030 da kuma shirin nan na dawwamamman ci gaba na (SDGs), kasancewar matasa su ne kashi biyu bisa uku na yawan al'ummar kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China