in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An ceto bakin haure 900 a yankin tekun dake dab da Libya
2017-06-17 11:45:01 cri
Sojojin tsaron teku na kasar Libya, sun ceto bakin haure 900 a yankin teku dake dab da Sabratsa, birnin dake yammanin kasar.

Kakakin sojojin Ayoub Qassem, ya shaidawa kamfanin dillancin labarun Xin Hua cewa, bakin hauren da aka ceto a jiya Jumma'a, sun hada da mata 98 da yara 25, yawancinsu kuma sun fito daga kasashen Larabawa da kasashen Afirka dake kudu da hamadar Sahara, inda suka yi shirin zarcewa Turai, amma sai jirgin ruwan su ya samu matsala.

Hukumar kula da harkokin bakin haure ta duniya ta bayyana a wannan rana cewa, tun daga farkon shekarar nan, an ceto bakin haure sama da 9,000 a yankin tekun Libya.

Tun bayan shekarar 2011 ne aka samu tabarbarewar tsaro a kasar Libya, al'amarin da ya sa gwamnatin kasar ba ta iya gudanar da harkokin bakin teku.

Kuma wannan ne ya sa wasu bakin haure da suka fito daga kasashen Afirka dake kudu da Sahara mai da Libya wata hanya ta tsallake Bahar Rum domin zuwa Turai. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China