in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: dole kasar Sin ta kyautata kwarewarta wajen kare muradunta a ketare
2017-04-27 13:34:25 cri

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya ce, dole ne kasar Sin ta kyautata kwarewarta a fannin tsaron kanta, a kokarin kiyaye hakkokinta a sassa daban daban na duniya yadda ya kamata, tare da ba da gudummowa wajen kare zaman lafiya a duniya da ma shiyya-shiyya.

Ministan ya fadi haka ne a jiya yayin da yake amsa tambayoyin manema labaru dangane da yadda jirgin ruwan yaki na farko da jiragen saman yaki ke sauka a kansa da kasar Sin ta kera da kanta ya shiga teku, a yayin taron manema labaru da ya yi da mataimakin shugabar kasar Jamus kuma ministan harkokin wajen kasar mista Sigmar Gabriel a birnin Berlin a wannan rana.

Wang Yi ya kuma jaddada cewa, akwai wani abu da kowa ya sani, kuma ba za a sauya shi ba, wato kasar Sin za ta ci gaba da mai da hankali kan tsaron kasa, a maimakon kai hari, kuma ba ta da aniyar mamaye wasu kasashe. Kasar Sin na kokarin raya huldar hadin gwiwa a tsakaninta da kasashen duniya don samun nasara tare. Tana kuma sa ran bullo da makomar bai daya cikin hadin gwiwar kasa da kasa. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China