in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fadar White House: Tattaunawar farko tsakanin Shugabannin kasashen Sin da Amurka zai inganta huldar dake tsakaninsu
2017-03-31 11:15:24 cri

Fadar White House ta ce shugaban Amurka Donald Trump na sa ran ganawa da takwaransa na kasar Sin Xi Jingping, da za ta inganta hulda a tsakaninsu.

Sanarwar da kasashen biyu suka bada a jiya Alhamis, ta ce Shugabannin biyu za su yi ganawarsu ta farko ne tun bayan da Trump ya kama aiki a watan Janairu, a fadar Mar-a-Logo na jihar Florida, a ranakun 6 da 7 na watan Afrilu.

Yayin wani taron manema labarai, kakakin fadar White House Sean Spicer ya ce, yayin ganawar ta Shugaba Trump da Shugaba Xi, za su yi masayar ra'ayoyi kan al'amuran da suka fi bawa muhimmanci da kuma inganta huldar dake tsakanin kasashensu.

Har ila yau, ya ce za kuma su tattauna, kan batutuwan da suka shafe su, ciki har da batun Koriya ta Arewa da cinikayya da kuma tsaron yankunansu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China