in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeria: an yi gargadi game da barkewar Cutar sankarau da zazzabin lassa a jihar Kano
2017-03-31 09:55:24 cri
Gwamnatin Jihar Kano dake arewa maso yammacin Nijeriya, ta gargadi al'ummar jihar su kara kula tare da rungumar matakan tsafta, bayan samun bullar cututtukan sankarau da zazzabin lassa a wasu sassan jihar.

Kwamishinan Lafiya na jihar Kabiru Ibrahim Getso, ya shaidawa manema labarai a jiya cewa, gwamnati ta inganta matakan sa ido a wasu kananan hukumomin jihar.

Ya kara da cewa, gwamnatin ta kuma dauki matakan da suka dace na takaita yaduwar cutukan, inda ya ce, an samu rahoton mutane 20 da suka kamu da cutar sankarau a kananan hukumomin jihar 8, inda daga cikinsu, mutane hudu ne kawai aka tabbatar da sun kamu da cutar.

Kabiru Getso ya ce ayarin masu kai daukin gaggawa na jihar ya sake fara aikin, yana mai cewa an kuma samar musu da magunguna.

Har ila yau ya ce gwamnati ta ba dukkan al'ummar jihar umarnin kara kula da yin taka-tsantsan, tare da gaggauta zuwa asibiti mafi kusa idan suka ji alamomin matsanancin ciwo kai ko zazzabi ko amai ko kuma rikewar wuya.

Bugu da kari, Kwamishinan lafiyar ya ce an bude layukan sadarwa domin taimakwa wajen takaita yaduwar cutukan, inda kuma ake wayar da kan mutane game da alamominsu ta kafafen yada labarai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China