Yau Jumma'a ne Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya sanar da cewa, Alain Aimé Nyamitwe, ministan harkokin waje da dangantaka da kasashen waje na kasar Burundi zai kawo ziyara kasar Sin daga ranar 13 zuwa 19 ga wannan wata. (Tasallah Yuan)