Sanarwar ta sake nanata cewa, gwamnatin kasar Gambiya na mutunta cikakken yankin kasar Sin, kuma ta yi alkawarin cewa, ba za ta kulla duk wata dangantaka da Taiwan ba, haka kuma ba za ta yi mu'amala da ita a hukumance ba.
A ranar 17 ga watan Maris din bara ne a birnin Beijing, ministocin harkokin wajen kasashen Sin da Gambiya, wato Mista Wang Yi da Madam Neneh MacDouall-Gaye suka rattaba hannu kan wata hadaddiyar sanarwa, dangane da farfado da dangantakar jakadanci tsakanin Jamhuriyar Jama'ar kasar Sin da Jamhuriyar Gambiya, kuma tun daga wancan lokaci ne suka dawo da dangantakar diflomasiyya dake tsakaninsu.(Murtala Zhang)