A shekarar 2016, kwamitin tsakiya na jam'iyyar Kwaminis ta Sin da majalisar gudanarwar kasar suka gabatar da shirin inganta harkokin kiwon lafiya a kasar Sin nan da shekarar 2030", wannan wani mataki ne na kokarin da ake na inganta harkokin kiwon lafiya a kasar Sin a cikin shekaru 15 masu zuwa, inda aka gabatar da ayyuka da matakai da za su farfado da sha'anin maganin gargajiya na kasar Sin da bada hidimar kiwon lafiya a kasar. (Zainab)