in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakiyar firaministan Sin ta yi kira da a kara hada kai a bangaren dakunan ajiye kayan tarihi
2016-11-11 09:26:34 cri

Mataimakiyar firayin ministan kasar Sin Liu Yandong ta yi kira ga kasashen duniya da su kara hada kai, tare da yin musaya a bangaren dakunan ajiye kayan tarihi.

Madam Liu ta yi wannan kiran ne a jiya Alhamis lokacin da ta ke jawabi a bikin bude taron dandalin dakunan kayan tarihi na kasa da kasa da ya gudana a birnin Shenzhen dake lardin Guangdong a nan kasar Sin. Bayanai na nuna cewa, ana baje kolin muhimman kayayyakin tarihi a irin wadannan dakunan ajiye kayan tarihi har sau 20000 a ko wace shekara, inda baki daga sassan duniya daban-daban kimanin miliyan 700 suke ziyarta, baya ga muhimmayar rawar da dakunan ke takawa wajen bunkasa harkokin jin dadin jama'a da na tattalin arziki.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China