in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kara kudi wajen habaka masana'antun al'adu
2014-08-27 10:47:15 cri

Ma'aikatar al'adu ta kasar Sin tare da ma'aikatar kudi za su hada hannu waje daya domin habaka wurare na musamman a bangaren masana'antun al'adu.

Kasar Sin za ta karfafa kokarinta a bangaren taimakon kudi, kafa shirye-shirye, da kuma jawo hankalin al'umma daga kasashen waje wajen kawo ziyara domin inganta tarihi da al'adun wasanni, kamar yadda aka sanar cikin wata takardar jerin shirye-shirye na ma'aikatun biyu a ranar Talatan nan.

Sin za ta mai da hankali a kan shigar da al'adun kasar a wajen gina birane da taimakon tsarin gine-gine na wuraren kasuwanci wanda zai nuna yanayin gidajen na karkara.

Kasar ta Sin har ila yau za ta ba da kwarin gwiwwa a kwalejoji, cibiyoyin bincike da hada-hadar ciniki da zai inganta hadin gwiwwa da kasuwannin cikin gida, in ji takardar jerin shirye-shiryen. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China