in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta gyara tsarin albashin ma'aikatan lafiyar kasar
2016-11-09 10:09:32 cri

Mahukuntan kasar Sin sun lashi takwabin gyara tsarin albashin ma'aikatan lafiya na kasar, a wani mataki na samarwa 'yan kasar ingantacciyar tsarin kiwon lafiya.

Babban ofishin kwamitin tsakiya na JKS da majalisar gudanarwar kasar mai kula da nasarorin da aka cimma a fannin yin gyare-gyare a bangaren kiwon lafiyar kasar ne suka gabatar da wannan shawara.

Manufar daukar wannan mataki, a cewarsu ita ce, karfafa gwiwar ma'aikatan lafiyar, ta yadda za su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Bugu da kari takardar shawarar ta bayyana cewa, za a bullo da tsarin da jama'a za su rika tantance kwazon ma'aikatan lafiyar, matakin da zai iya kai su ga samun karin albashi.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China