in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta dauki mataki kan masu damfara ta hanyar sadarwa
2016-11-08 11:37:21 cri
Sashen kula da harkokin sadarwa na kasar Sin ya fara nazari game da daukar matakai kan wadanda aka samu da laifin yin damfara ta hanyoyin sadarwa, a wani yunkuri na dakile aniyar masu amfani da hanyoyin sadarwar wajen yin almundahana.

A wata sanarwar da ma'aikatar kula da kamfanoni da fasahar sadarwa ta kasar Sin (MIIT) ta fitar, ta ce, za'a sanar da sunayen kamfanoni ko daidaikun jama'a da aka samu da laifin yin damfara ta hanyar kafofin sadarwa.

MIIT ta bukaci kamfanoni da su dakile duk wani yunkuri na masu yin damfara ta kafofin sadarwa da zarar 'yan damfarar suka bukaci aikata hakan.

Zuwa karshen shekarar nan ta 2016, kamfanonin sadarwa za su tabbatar da kammala yin rijistar masu ta'ammali da su na hakika.

Wannan mataki ya biyo bayan samun kiraye kiraye ne na neman daukar matakai kan masu aikata zamba da yin damfara ta hanyoyin sadarwa na zamani a fadin kasar, lamarin da ke haddasa yawaitar hasarar dukiyoyin jama'a.

A shekarar 2015, kasar Sin ta yi nasarar gano masu aikata damfara ta hanyar kafofin sadarwa sama da dubu 590, wadanda suka damfari kudi da ya kai RMB yuan biliyan 22.2, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 3.3. (Ahamd Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China