in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta Kudu ta nuna yabo kan dangantakarta da Habasha da Kenya
2016-11-08 10:18:26 cri

Kasar Sudan ta Kudu ta bayyana a ranar Litinin cewa, Kenya da Habasha, kasashe ne makwabtaka na gabashin nahiyar Afrika, kuma sun taimaka matuka wajen kulla yarjejeniyar zaman lafiya da aka sanya wa hannu domin kawo karshen rikicin da Sudan ta Kudu ke fama da shi a cikin shekaru biyu.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sudan ta Kudu, mista Mawien Makol Arik, ya bayyana a birnin Juba, cewa ziyarar faraministan kasar Habasha Hailemariam Desalegn a ranar 28 ga watan Oktoba, da muhimmiyar rawar da kasar Kenya ta taka a cikin kokarin gina zaman lafiya da kuma goyon bayan gina ayyukan kare fararen hula, sun kasance muhimman abubuwa wajen kafa huldar danganataka mai karfi tare da wadannan kasashe. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China