in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon ya yi maraba da zartas da sabon kundin tsarin mulkin kasa na Cote d'Ivoire
2016-11-03 13:24:26 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-Moon ta bakin kakakinsa ya bayar da wata sanarwa, inda ya yi maraba da sabon kundin tsarin mulkin kasa da Cote d'Ivoire ta zartas, ya kuma yi kira ga jam'iyyu daban daban na kasar da su guji amfani da nuna karfin tuwo ko furta kalaman da za su harzuka jama'a.

A cikin sanarwar Ban ya ce, kasar Cote d'Ivoire ta zartas da sabon kundin tsarin mulkin kasar ne bayan jefa kuri'ar raba gardama a ranar 30 ga watan Oktoba. A cewarsa, wannan zai taimaka wajen sassauta yanayin da kasar ke ciki, da kawar da bambanci a tsakanin bangarori daban daban.

Baya ga haka, Ban ya kalubalanci bangarori daban daban na kasar da su kawar da bambance-bambancen da ke tsakaninsu ta hanyar da kundin tsarin mulkin kasar ya tanada, kana da gudanar da tattaunawa da nufin shirya zaben majalisar dokoki a makwanni masu zuwa yadda ya kamata. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China