in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gamayyar kasa da kasa sun yi kira da a kara ba da kariya ga dabbobin daji da tsire-tsire dake bakin bacewa daga doron duniya
2016-09-25 16:56:10 cri
An bude taron kasashen da suka daddale yarjejeniyar cinikayyar kasa da kasa kan dabbobin daji da tsire-tsire dake bakin karewa karo na 17 a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu a ranar 24 ga wata.

Mahalarta taron a wannan karo sun kasance mafi yawa tun shekaru 43 da aka kulla yarjejeniyar, inda wakilai kimanin dubu 3 daga kasashe da yankuna fiye da 170 da hukumomin kasa da kasa fiye da 200 suke halartar taron wadanda kuma a tsawon kwanaki goma sha biyu za a tattauna batutuwa kimanin 120, da suka shafi batun kayyade cinikin dabbobin daji da tsire-tsire dake bakin karewa, kafa dokoki da gudanar da ayyuka bisa dokoki, tsara manufofin raya wannan fanni da dai sauransu.

Gwamnatin kasar Sin ta tura tawagar wakilai daga hukumomi da kungiyoyin da abin ya shafa don halartar taron, kuma shugaban tawagar shi ne mataimakin shugaban hukumar kula da harkar daji ta kasar Sin Liu Dongsheng. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
ga wasu
v Sin ba za ta amince da cinikin hauren giwa ba 2015-02-26 20:14:24
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China