in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WFP zai kara samar da tallafi ga mutane sama da miliyan 1.5 a yankin tafkin Chadi
2016-09-16 11:59:57 cri
Shirin samar da abinci na duniya ko WFP a takaice ya bayyana a jiya Alhamis cewa, zai kara samar wa mutane sama da miliyan 1 da dubu 500 da ke matukar bukatar tallafin abinci a yankin tafkin Chadi, yayin da ake kara samun wasu yankuna masu wahalar shiga a Najeriya.

Kakakin MDD Stephane Dejarric wanda ya bayyana hakan ga manema labarai, ya ce MDD ta yi kiyasin cewa, akwai mutane sama da miliyan guda da ke matukar bukatar agajin abinci a yankin na tafkin Chadi sakamakon rikicin Boko Haram.

WFP ya ce yana bakatar a kalla dala miliyan 72 nan da watanni 6 masu zuwa domin ya ci gaba da gudanar da ayyukansa na samar da abinci da sauran abubuwa masu gina jiki ga mutanen da suka bar muhallansu da ma masu daukar bakuncinsu.

Bayanai na nuna cewa, yankin tafkin Chadi dai ya kunshi kasashen Chadi da wani bangare mai girma na Jamhuriyar Nijar kuma yana daga cikin yankunan tafkuna masu girma a nahiyar Afirka. Kuma bai yi iyaka da kowane teku ba. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China