in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude rumfunan zaben raba gardama a Zambia
2016-08-11 14:51:41 cri

Al'ummar kasar Zambia, sun fara kada kuri'u a babban zaben kasar, da kuma zaben raba gardamar gyaran kundin mulkin kasar. An dai bude runfunan zaben kasar ne da misalin karfe 6 na safiyar Alhamis din nan. Ana kuma sa ran 'yan kasar miliyan 6.7 ne za su jefa kuri'u, a rumfuna 7,700 dake sassan kasar daban daban.

Zaben na wannan karo ya kunshi na shugaban kasa, da 'yan majalissun dokoki 156, da wakilan kananan hukumomi 1,624, da na magajin garin yankuna, baya ga na raba gardama kan kwaskwarimar da ake fatan yiwa kundin mulkin kasar.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China