in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana ta yi wa tawagar 'yan wasannin Olympic fatan alheri
2016-08-09 11:03:51 cri
Ministan harkokin wasanni na kasar Ghana Edwin Lantey Vanderpuye, a jiya Litinin ya aike da sakon fatan alheri ga tawagar 'yan wasan kasar dake halartar wasannin 2016 Olympics a birnin Rio de Janeiro, na kasar Brazil, a yayin da Ghana ta fara wasanninta.

Dan wasan kasar Kaya Adwoa Forson, mai shekaru 14, ya kasance dan kasar Ghana na farko da ya shiga gasar ninkaya a wasannin a katafaren filin ninkaya na Rio a ranar 8 ga watan Augusta.

Vanderpuye ya ce yana matukar alfahari kasancewar kasar Ghana tana daga cikin wadanda ke halartar wasannin na kasa da kasa, ya bayyana kyakkyawar fata ga tawagar 'yan wasan kasar da cewar, za su samu babbar nasara a gasar wasannin na Rio.

A sakon da ya gabatar a madadin shugaban kasar John Dramani Mahama, Vanderpuye ya bayyana cewar, ya kamata tawagar 'yan wasan su tuna cewar suna wakiltar al'ummar kasar Ghana ne baki daya, kuma jama'ar kasar gaba daya sun zuba musu ido.

Sannan ya bukace su da su tsaya tsayin daka domin ganin hakarsu ta cimma ruwa, kuma su nuna kyawawan halayansu.

Tawagar 'yan wasan na Ghana ta kunshi 'yan wasannin 16 wadanda suka halarci gasar wasannin na Olympic a karon farko, inda za su shiga wasannin nau'i 5 a gasar wasannin ta Rio.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China