in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Benin ta yi kira da a yaki cin hacin zabe a shiyyar yammacin Afrika
2016-07-14 11:18:46 cri
Ministan shari'a na kasar Benin, Joseph Djobenou, ya yi kira a ranar Laraba a Cotonou, ga mambobin kungiyar hukumomin kasa na yaki da cin hanci a yammacin Afrika (RINLCAO), da su fadada kwarewarsu kan yaki da cin hanci ta fuskar zabe a shiyyar yammacin Afrika.

A cewar jami'in, a lokacin da wani shugaba ya kama iko bisa turbar cin hanci, zai yi masa wuya sosai ya yi aiki bisa dokokin kasa a gaba. Yaki da cin hanci ta fuskar zabe a cikin kasashen yammacin Afirka, shi ne wani aiki mai muhimmanci da za a kula da shi bisa tsarin demokaradiyya na kasashen, in ji Joseph Djobenou.

Da yake magana a lokacin bude taron shekara shekara na RINLCAO, minista Djobenou, ya nuna cewa cin hanci annoba ce da ake samu ko ina, a nahiyar Afrika, har ma a dukkan kasashen duniya.

Matsalar ta zama ga al'umma da kasashe, kamar yadda ciwon kansa yake ga jikin dan adam. Duk da jajircewa da kokarin da ake yi domin kawar da shi, har yanzu yana bazuwa a cikin kasashe daban daban inda yake janyo illa sosai ga mutane, musammun ma ga masu zuba jari, in ji jami'in kasar Benin. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China