Congo Brazzaville ta yi kira da a warware batun tekun kudancin kasar Sin ta hanyar yin shawarwari cikin lumana
Gwamnatin kasar jamhuriyyar Congo Brazzaville ta bayar da sanarwa a daren ranar 20 ga wata, inda ta yi kira ga kasashen da batun tekun kudancin kasar Sin ya shafa da su warware batun ta hanyar yin shawarwari bisa tushen fahimtar juna,kuma ba tare da tsoma baki daga kasashen waje.
Sanarwar ta bayyana cewa, a ganin gwamnatin Congo Brazzaville, kamata ya yi bangarori daban daban su gano bakin zaren warware batun cikin lumana, bisa ka'idojin sanarwar ayyukan bangarori daban daban da batun tekun kudancin kasar Sin ya shafa da kuma tsarin yarjejeniyar dokokin teku na MDD. (Zainab)