in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka rasu sakamakon babbar gobara a wani gidan ibadar India ya karu zuwa 102
2016-04-10 18:33:05 cri
Shugaban jihar Kerala dake kudu maso yammacin kasar India, Oommen Chandy ya bayyana a yau 10 ga wata cewa, gobarar da aka samu a safiyar ranar a wani gidan ibadar addinin Hindu na jihar ta haddasa rasuwar mutane 102, tare kuma da raunatar 280.

Kafofin watsa labaru na wurin sun ruwaito bangaren 'yan sanda na cewa, gobara ta tashi da misalin karfe 3 da minti 30 a safiyar ranar, kuma mai yiwuwa ne gobara ta auku sakamakon kayayyakin wasan wuta da aka ajiye a gidan ibadar da za a amfani da su a yayin biki. An ce, kafin haka 'yan sanda sun taba gargadin wannan gidan ibadar game da amfani da kayyakin wasan wuta.

Bisa labarin da aka samu, ya zuwa ranar 10 ga wata da karfe 7 na safe, an riga an samu nasarar kashe gobarar. A yayin lamarin ya faru, akwai mutane dubu 10 zuwa 15 da suke cikin gidan ibada. A yanzu haka ana ta samun rasuwar mutanen da suka jikkata, yawancinsu kuma mata ne da yara kanana. Yanzu an riga an kai masu rauni a asibitoci don samun jinya. Bangaren soja kuma ya aika da jiragen sama masu saukar ungulu domin shiga aikin ceto. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China