Shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya kai ziyara a Rwanda
Bisa gayyatar da shugaban majalisar dattawan kasar Rwanda Bernard Makuza, da shugabar majalisar wakilan kasar Donatille Mukabalisa suka yi masa, mista Zhang Dejiang, shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, ya kai ziyarar aiki ta sada zumunta a kasar Rwanda takanin ranar 22 zuwa 23 ga watan nan, inda ya gana da shugaban kasar Paul Kagame, tare kuma da yin shawarwari da Mr. Makuza, da Madam Mukabalisa a birnin Kigali, fadar mulkin kasar. (Bilkisu)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku