in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban DPRK ya ce, kasarsa ta daidaita kundojin makaman nukiliya
2016-03-09 10:08:09 cri

Shugaba Kim Jong Un na Koriya ta Arewa ya bayyana cewa, kasar ta daidaita kundojin makamanta na nukiliya, ta yadda za su iya daukar makamai masu linzami.

Kamfanin dillancin labaran kasar KCNA ya ruwaito shugaban a yau Laraba, yana bayyana hakan lokacin da ya gana da ma'aikata da masana nukiliyar kasar, inda ya ba su umarni su kara inganta shirin makaman nukiliyar kasar.

Shugaba Kim ya sake yiwa masanan jawabi game da kara fito da dabaru da fasahohin kera makamai masu linzami wadanda za su rika amfani da kundojin makaman nukiliya, musamman kirar kasar ta Koriya ta Arewa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China