in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu 'yan kunar bakin wake biyu sun hallaka kan su a Kamaru
2015-12-28 20:04:47 cri
Wasu 'yan kunar bakin wake biyu sun hallaka kan su da sanyin safiyar Litinin din nan, yayin da suke shirin kaddamar da harin Bam a kauyen Bodo, dake yankin arewa mai nisa na kasar Kamaru. Rahotanni sun bayyana cewa baya ga maharan da suka rasa rayukan su, wani yaro daya ya samu rauni a sakamakon aukuwar lamarin.

A cewar wadanda suka ganewa idanun su wannan balahira, maharan mata ne da ake zaton magoya bayan kungiyar Boko Haram ne, sun kuma yi nufin kaddamar da harin ne kan fararen hula, sai dai a lokacin da mazauna kauyen suka gano su sai suka arce, sakamakon hakan ne kuma ya sabbaba tashin bama-baman da ke jikin su.

A daya hannun kuma, wata majiyar sojojin kasar ta Kamaru, ta ce wata 'yar kunar bakin waken na daban ta tarwatsa kan ta, tare da jikkata wasu mutum biyu a ranar Lahadin karshen makon jiya, yayin da Bam din dake jikin ta ya fashe a Tolkomari dake yanki na arewa mai nisa, mai makwaftaka da iyakar kasar da Najeriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China