in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar shiga tsakani ta sha alwashin samar da zaman lafiya a gabas ta tsakiya
2015-10-01 13:40:50 cri
Tawagar samar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya wato Quartet, ta jaddada kudurinta na gudanar da wani zagayen tattauna da nufin warware rikicin da yaki ci yaki cinyewa tsakanin Isra'ila da Palasdinawa.

Tawagar ta Quartet ta kunshi jami'an diplomasiyya da suka hada da na MDD da kungiyar tarayyar Turai EU da na kasashen Rasha da Amurka, wadanda ke samun goyon bayan sauran kasashen duniya domin tabbatar da zaman lafiya tsakanin Isra'ila da al'ummar Palastinawa.

Quartet, ta nanata cewar, akwai bukatar kasashen duniya su ba da gudumawarsu a kokarin da ake na samar da kyakkyawan yanayi wanda zai tabbatar da zaman lafiya a tsakanin bangarorin biyu.

Wannan sanarwa ta zo ne, bayan wata ganawa tsakanin babban sakataren MDD Ban Ki Moon da ministan harkokin wajen Rasha Sergey Lavrov da sakataren harkokin wajen Amurka John Kerry da kuma wakilin EU Federica Mogherini, kuma sun yi ganawar ne a lokacin babban taron MDD. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China