in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Benin na zaman makoki na kwanaki uku domin girmama 'yan kasarta da suka mutu a Mina
2015-09-27 10:31:17 cri
Kasar Benin na zaman makoki na kwanaki uku a dukkan fadin kasar tun daga ranar Asabar domin girmama mahajjatan kasar da suka mutu a sakamakon turmutsitsin da ya faru a ranar Alhamis din da ta gabata a Mina dake kusa da birnin Makka.

A tsawon wadannan kwanaki uku, tutocin kasar za su kasancewa zuwa rabin sanda a dukkan fadin kasarta Benin, kuma za a gudanar da salloli da adu'o'i a cikin masallatan mabiya addinin Musulunci domin nuna girmamawa ga mamatan. A cewar wata majiya ta kusa da sakataren kwamitin shirya hajjin shekarar 2015 na kasar Benin, mahajjatan Benin kusan goma ake tsammanin sun mutu, yayin da kuma wasu kusan satin aka rasa duriyarsu, daga cikin kimanin 'yan kasar Benin dubu hudu dake aikin hajjin shekara ta 2015 a kasar Saudiyya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China