Shekarar da muke ciki, shekara ce ta cika shekaru 10 da kulla dangantakar abokantaka bisa mayan tsare-tsare tsakanin kasashen Sin da Najeriya. A daidai wannan lokaci, ofishin jakadancin Sin dake Najeriya tare da hukumar raya al'adun gargajiya ta tarayyar Najeriya suka shirya wani biki a Abuja, tare da zummar nuna nagartattun al'adu na kasashen biyu.