in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rwanda na nuna damuwa kan yawan 'yan gudun hijirar Burundi
2015-04-18 16:16:42 cri
Kasar Rwanda na nuna damuwa da fargaba kan kwararar 'yan gudun hijirar Burundi a cikin kasarta, a yayin da kasar ta Burundi ke shirye shiryen zabukan shugaban kasa da na 'yan majalisu a cikin watan Mayu da Yuni na wannan shekara.

A cewar ma'aikatar dake kula harkokin 'yan gudun hijiri da bala'u, yawan 'yan gudun hijirar Burundi dake kasar Rwanda ya cimma dubu 6.571 a ranar Laraba da yamma, idan aka kwatanta da na dubu hudu a makon da ya gabata, kuma yawancinsu yara kanana ne. Mista Antoine Ruvebana, sakataren dindindin a ma'aikatar kula da 'yan gudun hijira da bala'u, ya bayyana wa manema labarai a ranar Jumma'a cewa adadin na ci gaba da karuwa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China