in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta taya Buhari murnar lashe zaben shugaban Najeriya
2015-04-03 18:54:48 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin madam Hua Chunying ta bayyana cewa, kasar Sin na taya Buhari murnar lashen babban zaben shugabancin kasar Najeriya da ya gudana a karshen makon jiya.

Madam Hua Chunying ta bayyana hakan ne a yayin wani taron menama labaru da aka shirya a yau Jumma'a, inda ta ce, mahukuntan kasar Sin na mai da hankali kwarai ga bunkasa huldar dake tsakanin kasar da kasar Najeriya.

Ta ce, bana shekara ce ta cika shekaru 10 da kafa huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen biyu, kuma bangaren Sin yana fatan hadin kan Najeriya, ta yadda sassan biyu za su kokarta tare wajen karfafa zumuncin gargajiya, da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu a fannoni daban daban, ta yadda za a iya kara ciyar da huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen biyu zuwa matsayi na gaba. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China