in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Namibiya ta gayyaci Ban Ki-moon halarta bikin rantsar da shugaban kasa
2015-03-17 09:54:09 cri

Sakatare janar na MDD, Ban Ki-moon, ya samu goron gayyata domin halarta bikin cikon shekaru 25 da samun 'yancin kasar Namibiya da kuma bikin rantsar da shugaban kasar na uku, Hage Geingob a ranar Asabar mai zuwa a Windhoek.

Ya zuwa dai wannan ranar, shugabannin kasashe goma ne suka tabbatar da zuwansu a bikin da za a shirya a babban filin wasan kasar.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, gwamnatin kasar ta bayyana cewa, za a tabbatar da tsaron dukkan shugabannin kasashen da aka gayyato, kuma ba za su bukatar zuwa da jami'an tsaronsu da za su kiyaye lafiyarsu ba. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China