Ya ce gwamnati na daukar karin matakan inganta harkokin ilimi ta hanyar ba da karin tallafi, a wani mataki na karfafa gwiwar al'ummun dake kwarara zuwa birane su iya komawa yankunan su.
Ya ce, hakan zai baiwa wadannan yankuna, damar ba da tasu gudummawa a fannin bunkasa tattalin arzikin kasar ta Sin. Daga nan sai ya bukaci wadannan yankuna da su fid da sabbin dabarun inganta masana'antu, tare da baiwa sabbin sassan samar da ci gaba kulawar da ta dace.(Saminu)